Daga Latifa Shuaibu Gani
Sanata Muhammad Ali Ndume da ke wakiltar jihar Borno ta Kudu a Majalisar Dattijai ya bayyana goyon bayansa ga shawarwarin da kungiyar gwamnonin Najeriya ta bayar kan sabuwar dokar haraji, sai dai ya ce har yanzu akwai wasu sashin dokar da zai yi kyau a ƙara yi wa jama’a bayani akai.
- Da Ɗumi-Ɗumi: An sake samun ɓullar wata sabuwar ƙungiya mai hatsari a Najeriya
- Gwamnan Neja ya haramta wa manyan motoci hawa saman gadar Dikko
- Dokar Haraji: Matakin da gwamnoni su ka ɗauka bai wadatar ba- Sanata Ndume
- Gwamnan Osun ya yi afuwa ga wani matashi da aka yanke wa hukuncin kisa don ya saci kaza
- Da Ɗumi-Ɗumi: Kotu ta bayar da belin tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello
Ndume wanda shi ya fara sukar dokar a lokacin da aka gabatar da ita a majalisar dattijai, ya ce dokar za ta ƙara tagayyara talakawa maimakon ta kawo musu sauƙi matsin da su ke ciki.
Yayin wata hira da BBC Hausa, Sanatan ya ce matakin da gwamnoni su ka ɗauka abin a yaba ne, to sai dai akwai buƙatar a buɗe ƙofar faɗaɗa tuntuɓa tare da jin ra’ayin jama’a kafin a ɗauki matakin tabbatar da dokar a hukumance.