6.7 C
London
Tuesday, February 18, 2025

Da Ɗumi-Ɗumi: An sake samun ɓullar wata sabuwar ƙungiya mai hatsari a Najeriya

Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (Nigeria Immigration Service) ta ja hankalin al’umma dangane da ɓullar wata ƙungiya mai suna “ACHAD Life Mission International” da ake zargi fa safarar mutane zuwa wajen ƙasar tare da raba yara da iyayen su.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a ranar 14 ga watan Janairun da mu ke ciki, ta ce ƙungiyar yanzu haka ta kafa hedikwata a Kaduna yayin da shugabanta, wani mai suna Mista Yokana, ke zaune a Jos na jihar Plateau.

Takardar Sanarwar da Hukumar ta fitar.

Ita dai wannan ƙungiyar kamar yadda sanarwar ta ce ba ta yadda da addinin Musulunci ko Kiristanci ba, amma ta na yaɗa da’awar dawo da al’adar nahiyar Afirka tare da taimaka wa al’umma.

Sabbin Labarai
Labarai Masu Alaka

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here