Monday, September 25, 2023
GidaLabarun GidaCikin kwanaki 100 mun ga irin kamun ludayin shugabancin Kauran Gwandu- Majalisar...

Cikin kwanaki 100 mun ga irin kamun ludayin shugabancin Kauran Gwandu- Majalisar Dokokin Kebbi

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta nuna goyon baya tare da amincewa da salon jagorancin gwamnan jihar Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) sakamkon irin nasarorin da ya samu cikin kwanaki 100 da hawansa kan karagar mulki.

Majalisar ta tabbatar bayyana hakan ne biyo bayan kudirin da aka gabatar a gabanta kuma dukkan ‘yan majalisar suka amince yayin zamanta a ranar Alhamis.

‘Yan majalisar sun nuna kwarin gwiwarsu akan gwamnan ganin yadda a cewarsu kwanaki dari ya dora jihar bisa turbar ci gaba musamman a fannin ilimi, lafiya, yaki da matsalar tsaro tare da samar da bababen more rayuwa.

Shugaban Majalisar Muhammad Usman Zuru ya kira ga sauran masu rike da mukaman siyasa da ma’aikatan gwamnati da su yi koyi da gwamnan ta hanyar maida hankali wurin gudanar da aikinsu yanda ya dace.

Isma'il Karatu Abdullahi
Isma'il Karatu Abdullahi
Isma'il Karatu gogaggen dan jarida ne da ya samu horo daga manyan kafafen yada labarai na duniya.
RELATED ARTICLES

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

Most Popular

Recent Comments