Monday, September 25, 2023
GidaDa Dumi-DumiDa Dumi-Dumi: 'Yan bindiga sun kashe sojoji 21 a jihar Neja

Da Dumi-Dumi: ‘Yan bindiga sun kashe sojoji 21 a jihar Neja

Akalla dakarun soji 21 ne suka mutu ciki har da manyan hafsoshi tare da raunata wasu ‘yan banga biyar a yayin wani gumurzu da da suka yi da ‘yan bindiga a garin Kundu da ke kusa da Zungerun a karamar hukumar Wushishi ta jihar Neja.

Rahotanni sun ce lamarin ya fara afku ne a ranar Lahadi, inda ‘yan bindigan suka kashe goma sha uku daga cikinsu sojojin a arangamar da suka yi da yayin da aka kashe wasu sojoji takwas a yau wani harin kwantan bauna, cikin wadanda aka kashe har da manyan sojin masu matsayin Kaftin da Manjo.

Wata majiya da ta nemi a saka sunanta ta shaida wa Hausa Daily Times cewa lamarin ya faru ne a lokacin da jami’an tsaron na kokarin tare hanyar da ‘yan ta’addan za su wuce bayan sun sato shanu da dama.

Majiyar ta kara da cewa, a asibitin Zungeru aka jibge gawarwakin sojojin ashirin da daya da aka kashe, kafin jirgin sojin saman Najeriya ya kwashesu zuwa Kaduna wanda shima daga bisani ya yi hatsari a wani kauye a karamar hukumar Shiroro duka a yau.

‘Yan banga biyar da suka samu raunukan harbn bindiga tare da sauran sojin da suma suka jikkata na karban magani a asibitoci daban-daban.

Har izuwa yanzu babu sanarwa daga rundinar Sojin Najeriya ko gwamnatin jihar Neja a hukumance dangane da wannan hari, sai dai rundinar sojin saman Najeriya ta tabbatar da afkuwar hatsarin jirgin samanta.

RELATED ARTICLES

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

Most Popular

Recent Comments