Thursday, September 21, 2023
GidaKunnen GariWaliyyin amarya ya sace sadaki ana tsaka da daurin aure a Kano

Waliyyin amarya ya sace sadaki ana tsaka da daurin aure a Kano

An zargi waliyyin ​​wata amarya da sace mata sadaki gabanin daurin auren a unguwar Kurna da ke karamar hukumar Dala ta jihar Kano.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da aka gano faruwar lamarin, an bar mutane cikin halin rashin tabbas game da daurin auren.

Wani mazaunin yankin mai suna Sunusi Dan Mamman ya shaida wa maniyar hausa Daily Times cewa bayan na tsawon lokaci, mahalarta daurin auren sun amince da a caji duk wanda yake zaune kusa da inda aka sace kudin.

“A yayin binciken ne aka gano kudin a cikin aljihun waliyyinta, wanda ya ce bai san yadda suka shiga aljihunsa ba.

“Da samun kudin, sai aka kori waliyyin daga masallaci saboda ba zai iya tsayawa amaryar a matsayin wakilinta ba, maimakon shi sai aka sa kaninsa ya bada aurenta daga nan aka co gaba da sha’anin biki”.

RELATED ARTICLES

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

Most Popular

Recent Comments