Monday, September 25, 2023
GidaLabarun GidaMarubuta mu ƙara jan ɗamara, Najeriya ta tuna da Abubakar Imam- Abubakar...

Marubuta mu ƙara jan ɗamara, Najeriya ta tuna da Abubakar Imam- Abubakar Abba Yakubu

Tashoshin jiragen sama 15 aka sanyawa sunayen wasu mashahuran ‘yan Najeriya.

Na yi murna da aka sanyawa filin jirgin saman Minna da ke Jihar Neja, sunan marigayi Malam Abubakar Imam, tsohon marubuci kuma ɗan jarida. Mawallafin littafin Magana Jari Ce, kuma Editan farko na jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo!

Ba lallai sai ka zama gwanin iya rubutu da turanci ba. Ɗaukaka ta Allah ce! Na san ba za mu taɓa mantawa da gudunmawar jagoran mu Alhaji Ado Ahamad Gidan Dabino, da ya samu shaidar yabo ta ƙasa ta MON, albarkacin rubutu da harshen Hausa.

Mu daina ƙyamar yin rubutu da harshen mu na gado, don kar a raina ilimin mu da wayewarmu!

Ga su nan:

  1. Akure Airport – Olumuyiwa Bernard Aliu
  2. Benin Airport – Oba Akenzua II
  3. Dutse Airport – Muhammad Nuhu Sanusi
  4. Ebonyi Airport – Chuba Wilberforce Okadigbo
  5. Gombe Airport – Brigadier Zakari Maimalari
  6. Ibadan Airport – Samuel Ladoke Akintola
  7. Ilorin Airport – Gen. Tunde Idiagbon
  8. Kaduna Airport – Hassan Usman Katsina
  9. Maiduguri Airport – Gen. Mumammadu Buhari
  10. Makurdi Airport – Joseph Sarwuan Tarka
  11. MINNA AIRPORT – MALAM ABUBAKAR IMAM
  12. Nassarawa Airport – Sheikh Usman Dan Fodio
  13. Osubi Airport – Alfred Diete Spiff
  14. Port Harcourt Airport – Obafemi Jeremiah Awolowo
  15. Yola Airport – Lamido Aliyu Mustapha
RELATED ARTICLES

BAR AMSA

Don Allah shigar da sharhinku!
Don Allah shigar da sunanka a nan

Most Popular

Recent Comments