Sabon Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya rantsar da sabbin Kwamishinoninsa guda 17.
A yayin bikin rantsuwar wanda ya gudana a babban dakin taron Majalisar zartaswar jihar, gwamnanya ce “muna taya sabbin kwamishinoni murna, da fatan za ku rike amana, kuma kada kudi ya rude ku, tare da fatan ba za ku shigar da iyalanku cikin aikinku ba.”