Wani matashi dan Kwankwasiyya kuma daya dava cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin karatu na gwamnatin tsohon Gwamnan Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya jaddada goyon bayansa gareshi tare da godiya bisa inganta zuri’arsu.

Matashin mai suna Abdulkarim ya bayyana a shafinsa na Twitter cewa, “Na gode @KwankwasoRM bisa sauya rayuwata da ka yi daga talauci zuwa ingantacciyar rayuwa. Ba tare da sanin kowa ba a Kano ka turani karatu kasar Egypt yau ga shi ina aiki a Ingila (England).

“Irin wadannan abubuwa su ne abin da mutanen Kano suke gani kuma suke ci gaba da godiya a gareka.